SHEHU IBRAHIM NIASSE(R.A) Yana Cewa:-

 



"Bushewar Zuciya, Itace Mafi Girma a Cikin Bala'i Bayan Kafirci. Akwai Ayyuka Guda 24 Dake Busar Da Zuciya, Wanda SHARI'A Bata Yarda Da Su Ba, 


*1 - Mutum Ya Tsaya Akan Zunubi Guda Daya, Yayi Tayi Yana Maimaitawa. 


*2 - Tsawon Buri, Mutum Ya Zama Bai Wadata Da Abinda ALLAH Ya Bashi Ba. 


*3 - Yawan Fushi, Ba Akan Tafarkin ALLAH Ba. 


*4 - Musulmi Ya Riqe Dan'uwansa Musulmi a Zuciya. 


*5 - Son Duniya Kota Halin Yaya. 


*6 - Son Girma, Cikin Kowane Hali.


*7 - Katsalandan a Harkar Da Ba Ruwanka a Ciki. 


*8 - Yawan Dariya, Mutum Ya Zama Kamar Wawa. 


*9 - Yawan Zolayar Mutane. 


*10 - Jindadi Saboda Abin Duniya, Har Kamanta Da ALLAH Saboda Farin Ciki. 


*11 - Baqin Ciki, Yayin Da Jindadi Ya Zo Ya Koma. 


*12 - Gafala Ga Barin Zikirin ALLAH. 


*13 - Rafkana Ga Barin Tunanin Lahira. 


*14 - Barin Yin Tunani Akan Sha'anin Wuta. 


*15 - Barin Yin Tunani Akan Sha'anin Aljannah. 


*16 - Yawan Yin Firar Banza. 


*17 - Yawan Yin Abota Da Wawaye. 


*18 - Da Yawan Cin Haram. 


*19 - Mugun Cin Abinci. 


*20 - Da Yawan Janyo Sha'awa. 


*21 - Yawan Barci


*22 - Yawan Tunanin Banza


*23 - Qarancin Ambaton ALLAH


*24 - Ji Da Kai, Ji Da Kai,


ALLAH YA TSARE MANA ZUCIYOYINMU DAGA BUSHEWA ELAHEEEY AMEEEN.


Islam Autar mama:-

Ma'asumah Nigerian News Update, Mnnu//Ng0027


Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post