murucin kan dutsae:- Daka manzon allah (s a w w)



Akwai Hadisai da dama da suka yi magana a kan

martabobi da darajojin Ahlul Baiti. Za mu takaita

kan wasu hadissai ingantattu guda bakwai (7).

Amma bari mu soma da waɗannan guda biyu

waɗanda suke bayyana fifikon dangin Annabi

(Sallalahu Alaihi Wasallam) baki ɗaya akan sauran

mutane.

Tirmizi ya rawaito falalar Annabi (Sallalahu Alaihi wa'alihi

Wasallam) cewa: Abbas (Allah ya ƙara masa

yarda) ya ce: “Na ce wa Manzon Allah (Sallalahu

Alaihi wa'alihi Wasallam), Ƙuraishawa sun zauna suna bitar

tarihin gidansu. Sai suka kwatantaka da muruccin

kan dutse. Sai Annabi (Sallalahu Alaihi wa'alihi Wasallam)

ya ce: “Da Allah ya tashi samar da halitta, sai ya

zabi mafi alherinta ya sanyo ni a ciki. Ya kuma zabi

mafi alherin ƙabilu ya sanyo ni a ciki. Ya kuma zabi

mafi alherin gidaje ya sanyo ni a ciki. Saboda haka

ni ne mafi alherinsu ga tushe da asali”

Zamu cigaba insha allah...1

Mnnu/Ng0027 Baban Humaid Ma'asumah tv Nigerian News Update

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post