Wasu Daga Cikin Halayen da Dabi'u na Imam Hassan Al-Mujtaha (As).



Asalin tanajin da aka tanada don Imam Hasan (a.s.) ya

tabbatarwa samuwarsa ta ruhi wata kololuwar daukaka.

Kusancinsa ga Allah da ta’allakursa da Shi wani al’amari

ne da ke girgiza zuciya kuma hankali ke mika wuya a kai.

Imam al-Sadik (a.s.) yana cewa:

“ Imam Hasan bin Ali ya kasance mafi bautan mutanen

zamaninsa, kuma ya fi su gudun duniya da daraja ”.

Haka nan ya zo cikin littafin Raudhatul-Wa’izina cewa:

“(Imam Hasan) Ya kasance idan yana alwala sai jikinsa ya

rika kakkarwa kuma launinsa ya canza, da aka tambaye shi

dalilin haka sai ya ce:

“ Hakki ne aka duk wanda ya tsaya a gaban Ubangijin

Al’arshi launinsa ya canza kuma gababunsa su kada ”.

Ya kasance idan ya isa kofar Masallaci ya kan daga kansa

ya ce:

“Ya Allah! BakonKa ke kofarKa. Ya Mai yawan kyautatawa

hakika, mai munanawa ya zo maKa, to Ka ketare munanan

abubuwan da ke gare ni da kyawawan abubuwan da ke

gare Ka, Ya Ma’abucin karimci ”.

Ya kasance idan yana karanta Alkur’ani, duk lokaci da ya

zo ayar da da ke cewa: (Ya ku wadanda suka ba da

gaskiya ) yakan ce: “ AmsawarKa! AmsawarKa!! Amsa-

warKa!!!

An ruwaito daga Imam al-Sadik (a.s.) cewa:

“ Imam Hasan bin Ali (a.s.) ya tafi hajji har sau 25 da kafa.

Ya kuma raba dukiyarsa biyu ya ba Allah rabi ”.

Kyawawan dabi’unsa kuwa wani abu ne mai misalta

dabi’un Alhlulbaiti (a.s.). Littafan tarihi sun hakaito cewa:

“Imam Hasan ya taba bi ta wajen wasu mutane matalauta,

a lokacin suna tsintar guntattakin gurasa da aka ci aka

rage kuma aka watsar a hanya, suna ci. Da suka gan shi

sai suka yi masa tayin ya zauna ya ci tare da su. Sai kuwa

ya amsa musu da cewa: ‘ Hakika Allah ba Ya son masu

girman kai.’ bayan da ya gama da su sai ya gayyace si

bakuntarsa, sai ya yalwata su da dukiya mai yawa, ya

kuma ciyar da tufatar da su”.

Wata rana an taba ce masa: “Me ya sa ba mu taba ganin

ka ki amsawa mabukacin da ya tambaye ka ba?” sai ya

amsa da cewa:

“ Hakika ni ma mai rokon Allah ne, kuma mai kwadayi gare

Shi; don haka ina kunyar in zama mai roko alhali kuma ina

hana mai roko. Kuma Shi (Allah) Ya sabar da ni da bayar

da ni’imarSa gare ni, haka ni ma na sabar da Shi in bayar

da ni’marSa (da Ya ba ni) ga mutane; to ina tsoron in na

yanke al’adata Shi ma Ya yanke al’adarSa ”.

Haka nan Imam Hasan (a.s.) ya taba sayen wani lambu

daga wasu mutane Ansarawa da kudi dirhami dari hudu,

sai labari ya zo masa cewa (wadanda suka sayar masa

din) sun koma suna bukata daga mutane, sai ya koma

musu da lambun ba tare da ya karbi kudinsa ba.

Wannan kadan ne daga daga siffofinsa (a.s.), kuma wani

bangare ne na matsayinsa tare da daidaikun wannan

al’umma. Dabi’unsa sun kasance mafi tasiri wajen misalta

kyawawan dabi’un Musulunci .


             Mnnu//Ng0027


Ma'asumah Nigerian News Update

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post