A Irin Wannan Rana ta 15 Ga Watan Ramadan Sayyadah Fatimah (sa) Ta Haifi Imam Hasan Al-Mujtapha (as).



A ranar sha biyar ga watan Ramalana mai albarka na

shekarar hijira ta uku, gidan Annabci ya sanar da haihuwar

jikan farko, nan take sai Manzon Allah (s.a.w.a) ya garzaya

zuwa gidan Fatima (a.s.) don sadar da taya murna da farin

cikinsa.

Bayan isowarsa, sai aka gabatarwa Manzo (s.a.w.a) da

abin haihuwa mai albarka, Manzo ya tarbe shi, ya dauke

shi a hannunsa, ya sumbace shi, ya rungume shi a kirjinsa;

sai kuma ya kira salla a kunnensa na dama, ya yi ikama a

na hagu da sautin gaskiya da ya zama farkon sautin da ya

fara ratsa samuwarsa da jinsa. Sai Manzo (s.a.w.a) ya

waiwayi Ali (a.s.) ya ce: “ Wane suna ka sa ma dana ? ” sai

Imam Ali (a.s.) ya ce: “Ban kasance mai shiga gabanka ba “,

sai Manzo ya ce: “ Kamar yadda ban kasance mai shiga

gaban Ubangijina ba ”. Wannan tataunawa ba ta kai

gacinta ba sai ga wahayin Allah na saukowa ga Manzo

(s.a.w.a), wanda ke sanar da shi cewa Allah Madaukaki Ya

sanyawa abin haihuwan suna Hasan .

Lokacin da kwanaki bakwai da haihuwa suka kewayo, sai

Manzo (s.a.w.a) ya sami rago ya yi masa akika (yankan

suna) da shi, daga ciki ya ba unguwar–zoman da ta karbi

haihuwarsa cinya tare da dinari guda, wannan a matsayin

godiya bisa kokarinta a madadin abin haihuwa da

mahaifiyarsa mai tsarki. Sannan ya kama kan abin haihuwa

ya aske, ya yi sadaka da nauyin gashin da azurfa wanda ya

yayyafe shi da (wani nau’in turare da ake kira da) Khaluk ;

sannan ya sa aka yi masa kaciya.

Wannan abu dai da Manzon Allah (s.a.w.a) ya yi a ranar

sunan Hasan (a.s) ya zamanto sunna da musulmi suke koyi

da ita.


             Mnnu//Ng0027


Ma'asumah Nigerian News Update

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post