MUHIMMANCIN ADDU'A A MAHANGAR AHLUL BAIT {AS}

 


                  (1)


Idan mutum yayi bincike Addu’a a

mahanga ta Ahlul bayt wato a bisa karantarwa

ta Ahlul bayt zai ga cewa Addu’oin da aka samo

daga Aimma na Ahlul bayt babu wani da aka

samo irinsu a wannan al’umma ta Manzon Allah

[S] wannan a bayyane yake duk wanda yayi

bincike zai ga haka misali mutum ya kwatanta

littafan Addu’oi da ake dasu a Shia da kuma

Sunna,wato zai ga cewa littafan Addu’oi a Shia

sun fi yawa kan na sunna,in mutum yayi tunani

zai ga cewa }ila wannan bai rasa nasaba da irin

halin da Aimma da kuma shi’arsu suka kasance

na jarabawowi dabam dabam tsakaninsu da

hukumomi da kuma jama’a na

zamunnansu.Saboda haka duk wanda yake

riyawar cewa yana bin Aimma na Ahlul bayt

amma yaga babu wata jarabawa da yake fuskanta

to ya binciki kansa ko dai ba tafarkinsu yake

biba.Saboda dukkan Aimma da mabiyansu sun

sha wahala an kuma cutar dasu ta fuskoki

dabam dabam,kai baki ]ayansu daga wanda aka

kashe sai wanda aka sa ma guba,kuma mutum

ya tambayi kansa idan Imam Mahdi[AF] ya

bayyana Gwagwarmaya zai yi domin tabbatar da

Addini ko zama zai yi ya ba da karatu shike nan?

Mu kuma duba tarihin Imam Khumaini yayi

gwagwamarya domin tabbatar da Addini ya

kuma ba da karatu.

Idan mutum ya bibiyi littafan Addu’oi zai

ga cewa addu’oi sun kasu kashi hu]u sune:

1-Na yaumiyya wato wa]anda ake karantawa

kowace rana,misali na safe da yamma ko na

bayan salloli da dai sauransu.

2-Na Usbu’iyya wato wa]anda ake karantawa

kowace rana cikin mako,misali na ranar

Jumma’a,Asabar,Lahadi……


Za'a cigaba insha allah



           Mnn//Ng0027


Ma'asumah Nigerian News Update

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post