Jami'an tsaron Nigeria Suna Shirin Shekar da jinin Yan uwa musulmi a garin Makarfi ta Jahar Kaduna

 



duba da yanda Labarai suka futa daga safiyar Jiya Juma'a 09/12/2022 Jami'an tsaro suna shirin aukawa yan Musulmi Almajiran Sheikh Ibrahim Zakzaky Hafizahullah dake garin Makarfi.

jami'an Sunyi wannan Shirin ne tun daga lokacin da yan uwan suka ai'yana cewa yau ne 10/12/2022 zasu gabatar da Muzaharar Maulidi ta bana a garin.

iya yanzu dai da safiyar nan sun jubge Jami'an a kowani Babban Hanyan garin da kuma titin garin

Sun kuma zagaye inda za'ayi taron Yanzu haka da safiyar nan 7:25am

karin dad'awa muna fadawa mutanan gari su sani mu zamu futo ne domin murnan Haihuwar Fiyayyan Halintta Annabin Rahma domin murna da sabuwarsa wanda mukeyi a duk shekara kuma wannan shekaran zamuyi insha Allah babu fashi.



Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post