Hadisai Goma (10) Daga Bakin Imam Musal Khazim (A.S)




`Ma'asuma Nigeria news update.

-Imam yace musiba ga wanda ya jure guda ɗaya ce, ga wanda kuma bai jure ba guda biyu ce, wato musibar da kuma radadin rashin dauri yar acikin zuciya.

-Imam yana cewa taimakonka ga raunana yana daga cikin mafificiyar sadaqa.

-Imam yace yawan damuwa da kuma baƙin ciki yana haifar da saurin tsufa.

-Imam yace rikon amana da kuma Faɗin gaskiya, suna janyo arzuki, yin karya da kuma yaudara suna janyo talauci da kuma munafunci.

-Imam yace mutun bai samun ladar musibar da allah T ya jaraba shi da ita face sai idan ya daure kan musibar.

-Imam yace kyakkyawan makwabtaka ba itace kawai kamewa daga cutar da makwabci ba, a'a itace daurewa daga cutar war makwabci.

-Imam yace na hore ku da yin addu'o, domin addu'a tana tunku de bala oi.

-Imam yana cewa duk wanda ya fara addu'a batareda soma yabon Allah T ba, Dakuma yima manzon Allah salati ba to kamar wanda yayi harbi ne da gwafa ba dutse.

-Duk wanda yakasance mai tattali to ba zaiyi talauci ba.

-Imam yace ku nemi ilimin addini saboda shi ilimi mabudin basira ne kuma dalili na zuwa ga madaukakan darajoji.

#Abbakar Labbo.
#Public health concern.

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post