Sabon Hari Rokoki A Sansanin Sojin Amirka A Kasar Iraki.

Daga Wakilin Mu --Idishia Jos. Hukomin tsaro a Iraki sun tabbatar da saukar manyan rokoki a kusa da sansanin sojojin Amirka da ke Bagadaza babban birnin kasar. An ji karar fashewa a yammacin gabar Tigris yankin da yawancin ofisoshin jakadancin kasashen waje suke a Iraki. Babu wadanda suka dauki alhakin sabbin hare-haren rokokin kan barikin sojojojin Amirka da ke Irakin zuwa yanzu. Sai dai dama ana zaman dar-dar na yiwuwar harin fansa daga Iran tun bayan da Amirka ta kashe janar Qassem Soleimani, wannan dai na zuwa ne a dai-dai lokacin da Jamus ta dawo da atisayen sojinta a Iraki bayan dakatarwar da ta yi. Daga Shafin Ma'asumah Nigerian News Updates.

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post