"Abin da zai zama abu mai dadi mai faranta rai shine, mun tabbatar har ga Allah, Amurka ba za ta iya cutan Musulunci ba! Duk abin da za su yi sai ya zamar ma Musulmi alkairi. Illa iyaka tana barazanar za ta kashe mutane. Shikenan kawai!

"To, sai mu ce Amerika ki yi duk abin da za ki yi, Allah mahaliccin sama-da-kasa ya fi karfinki. Wata kila ma karshenki ne ya zo. Ana tambaya ta ko karshen Amurka ne ya zo? Nace ya danganta da abin da suka yi. Sune dai za su kawo karshen kansu. Ya rage musu kuma.

"A sa lissafinmu a cikin 'yan ta'addan! A zo din, ai luguden wutan! In ce ko wannan rayuwar duniya suka sani ko? Illa iyaka abin da suka sani kenan. To mu mun san bayan wannan akwai wata rayuwa, wasunmu wannan (farmakin Amurka) zai zama musu sanadiyyar samun babban rabonsu na zuwa Aljanna (Shahada). To, kuma za a samu saura wadanda za su ragu, wanda a hannunsu Allah (T) zai kawo karshen Amurka, insha Allah.
"