JABIR BIN ABDULLAH DAN SAKON MANZON ALLAH (S) NE



Sannan kuma Jabir bin Abdullahil Ansari ya yi tsawon rai, ya yi zamani da Amirulmuminin (AS), ya yi zamani da Hasan da Husain (AS), ya yi zamani da Aliyu Binil Husaini (AS), sai a zamanin Ali Binil Husaini ne har ma ya ga haihuwar Imam Baqi (AS), har ma ya isar da sakon da Manzon Allah (S) ya aike shi izuwa Imam Baqir yana jariri.

Don Manzon Allah (S) ya fada masa A’imma 12, yace masa kuma za ka ga na biyar dinsu mai suna Muhammad wanda za a ma lakabi da Baqir, in ka ganshi kace ina gaishe shi. To kuma har sai da aka haifi Imam Baqir, sannan yace masa isar da sakon da Manzon Allah ya aike ka. Sannan ya isar da sako din.

Na san ba su da wannan ruwayar su Ahlussunnah, amma muna da shi mu. Yace Manzon Allah yana isar maka da ‘Salam’ (gaisuwa). Sai yace “Wa’alaihis Salam.” Kuma lokacin Imam Baqir yana jariri, amma yace “Wa’alaihis Salam Ya Jabir.” Sannan Jabir yace, na riga na isar da sakon nan, saura in tafi. Kuma bai dade ba ya rasu. To kaga shi Quduwa ne. Ko ba a lura ba?

             Mnnu//Ng0027

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post