ASALIN TATTAKIN ARBA’IN DIN IMAM HUSAINI (AS) :-cibiyar wallafa



To, shi Tattakin Arba’in ya yo asali ne tun shekarar farko na shahadar Abi Abdullah (AS). Arba’in din farko, wanda aka ce Jabir bin Abdullah al-Ansari (Radiyallahu Anhuma), shine farkon wanda ya kai ziyara na Arba’in. Ya dai kai ziyara ne, sai ya dace da ranar Arba’in a Karbala.

Ya tafi daga Madina, sannan da ya je sai ya sauka a bakin kogin Furat, ya yi wanka ya sanya tufafi masu tsafta, sannan ya bulbula turare, sannan ya taka da kafa ba takalmi, yana tafiya a hankali, cikin natsuwa da kuma yana Azkar, har ya isa makwancin Abi Abdullah (AS), ya dora hannunsa, ya kira shi da karfi har sau uku. Sannan ya fashe da kuka yana cewa, ina kiran masoyi na san masoyi na ji, amma ba zan ji amsar sa ba. Da wadansu kalamai dai masu sosa rai, wadanda suna nan a muhallinsu, idan mutum ya karanta.

Ana cikin haka nan, sai suka hango duhun wadansu mutane suna dimfaro wurin. Sai yace da wani bawansa, jeka ka duba mana ka ga wadancan masu zuwan su wane ne? In mutanen Ibn Ziyad ne sai mu samu wurin da za mu fake (wato su bar wurin, su je su samu mafaka kenan, su buya daga wadannan mutane). Yace, idan kuma Maulaya wa Sayyidi ne, Imam Zainul Abidin (AS) to.

To sai kuwa ta zama Imam Zainul Abidina ne ke tafe. Don lokacin da za a koma da su Madina, su suka bukaci a bi da su ta nan, duk da dai kasar Karbala daga Dimashq ba hanyar Madina take ba, an kara tafiya ne, amma su suka bukaci a yi musu haka nan, kuma aka yi musu haka nan din. Sai kuwa shi bawan nasa ya dawo yace masa, ai Maulana wa Sayyiduna Imam Zainul Abidin ne. Har (Jabir) yace masa, “Anta Hurru li wajhillah.” (kai ‘yantacce ne saboda Allah). Nan take ya ‘yanta shi saboda wannan albishir da ya yi masa.

To, sai ga shi Imam Zainul Abidin da Sayyida Zainabul Kubra (SA) da sauran iyalan Annabi (S) sun zo wannan muhalli, to nan suka hadu da Jabir Bin Abdullah al-Ansari. Imam Zainul Abidin yana cewa, ya Jabir, nan ne aka kayar da mazajenmu, nan ne aka fille kawuka dinmu. Maganganu masu sosa rai, duk aka yi ta kuka, aka yi ta koke-koke. To muna cewa wannan shi ne Arba’in na farko.

Zamu cigaba insha allah...
                  Mnnu//Ng0027

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post