MURUCIN KAN DUTSAE (2) Baban Humaid Mnnu/Ng0027

 

 Martabobi da darajojin manzon Allah

(S A w w)

Hadisi na

biyu da ya da 

 a fili, shi ne:

Imamul Muslimu ya ruwaito daga Wasilatu dan

Aska’u wanda ya ce: “Na ji Manzon Allah

(Sallalahu Alaihi wa'alihi Wasallam) na cewa: “Haƙiƙa Allah

ya zaɓi kinanata daga cikin ‘ya’yan Isma’il. Daga

cikin Ƙuraishawa kuma ya zaɓi Banu Hashim.

Daga cikin Banu Hashim kuma ya zave ni”. Muna

iya lura daga wadannan hadisai guda biyu cewa,

Manzon Allah (Sallalahu Alaihi wa'alihi Wasallam) an zabo

shine daga dangi zababbbu.

Don haka, duk wanda ya ke tunanin ya san darajar

Manzon Allah (Sallalahu Alaihi wa'alihi Wasallam) amma

bai san darajar danginsa ba, to bai gano asalin

Manzon Allah ba. Haka kuma za mu iya lura cewa,

Manzon Allah (Sallalahu Alaihi wa'alihi Wasallam) ya na

kula da zumunci na kusa da na nesa, ya na yi mu

su addu’a, kuma ya na yi wa musulmai wasicci da

su kaunace su, su kula masa da su, su kyautata a

matsayin wani haƙƙinsa a kan su...2


Zamucigaba insha allahu

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post