Tarihin Usman Dan Fodiyo, Cigaba Babi na 2



Ci gaba babi na 2

@_Mmaa'asuma Nigerian News Update


            Tare da Abokin Aikin Mu

EngMuhammad Hamza UsmanYarsakakea✍️


       WAAZINSA DA  KARANTARWAR SA


Tarihi ya tabbatar da cewa  tun shehu  Usmanu  yana dan shekara ashirin  yafara kiran mutane  zuwa ga hanyar Allah. Ana iya gani wannan kamar yadda malam abdullahi  ya rubuta  a cikin littafinsa maisuna Tazinul.  Muna iya raba waazin shehu  da karantarwarsa  zuwa gida biyu.


NADAYA


majalisarsa ta wa´azi  da shiryarwa. Bayani  zaizo nan gaba


NABIYU 


 majalisar koyarwa (ko karantarwa).Acikin  wannan zamane shehu  kan fita bayan sallar laasar  ko bayan sallar isha´i yana  fassarawa mutane Alkur anil,  yana karantar dasu hadisan manzon allah(s a w) da fikhu  da sufanci  da uaran fannoni na ilimi. Acikin wadannan darussa nasane  yake  yiwa mutane  bayani, gwargwadon fahimtarsu. darussa  nasa sunkasance  akan abubuwa  biyar. Nadaya bayani akan abubuwan da sharia  ta wajabta  na daga zahirin shari´a  da badininta. Maana  dai  akan binda  ake kira  shari`a  da hakika. Na biyu: sune darussa akan sunnar Manzo (s a w) da bincikenta  da kuma kwadai tarwa  daga bin umarninta. Na ukku  bincike akan ilimin tauhidi  da abinda ake kira ilimul kalami. Acikin wadannan  da russane  yake gyaran  kura kuran da dalibai  da marasa fahimta  ke kwaftawa  wannan fanni. Haka  a cikin  wannan majalisa ce yakan gabatarda  darussa akan  fannin fikihu  da gyaran hankulan dalibbai  dan ganeda wannan fanni da kuma mayar da su zuwaga abinda ya fi zama dai dai. Nahudu sube darussan da yakegabatarwa a gameda  gano  bubuwa  da aka kago  a kan jingina ga addini  alhali  kuwa su ba addini bane. Abin nufi  da wadannan su ne  bidi o i da al´adu  marasa  kyawo da aka jingina ga  addini . Wannan abu  a bayyane yake  ga duk wanda ya karanci littafan  shwhu kamar su Ih ya`u sunna   da Bayanul bidi´a i.  karin bayani  ga littafansa.  Wannan na nuna  shehu  na da majalisa  ta kawra da bidi o i da  al adu miyagu. Na biyar  sune darussan da yake  gabatarwa  danganeda  ilimin sharia  da binciken manyan matsaloli  flla filla  da kuma ilmantarda dalibai  akan manyan matsaloli  baki da kawar musu da duk abinda ke damunsu.  Wannan na nuni ne ga  yadda shehu  ke baiwa manyan dalibai  ilimi  da yadda yake  dorasu  akan matakan da suka dace  dasu. Wadannan sune kadan daga  cikin  abubuan da shehu  ya koyar da dalibansa  da masu saurarensa  manema ilimi kowane an koyardashi gwargwadon matakinsa. Akan 6angare  nabiyu watau majalisar waazi (ta shehu) sarki muhammadu bello  yarubuta  littafi na musamman  mai suna attar jumanu an kaifiyyati.Waazi  shaykhu usmanu. Akansa  yayi bayanin yadda  shehu usmanu ke yin waazi haka kuma yazo da irin wannan bayani  a cikin littafinsa na infaku. sarkin musulmi muhammadu bello  ya nuna cewa  abinda shehu  ke bayninsa ga mutane  a majalisarsa  ta waazai bai shige abubuwa ukku ba.  1.bayani akan asalin addini watau tauhidi.

Aciki wannan darasi  ne ya yake bayani  bayani akan ilahiyyatu. Bayani akan abubuwan da yakamata ko ya wajaba  mutum ya kudurta  danganeda kadaita Allah,  wanda  shine ilahiyyatu. Bayani  akan abubuwanda  yakamata ko ya wajaba  ya kudurta danganeda annabawa  da manzanni  wannan kuwa  shine  Nabawiyyatu. Haka  kuma  da bayanai  akan abubuwanda ake ji  amma baa ganinsu  na daga al amarin lahira  kamar bayani  gameda wuta da aljanna  da suaransu. Wannan  kuwa shi ake kira  sam iyyatu.  shehu  usmanu  yayi littafi na musamman  dangane da  wannan sunan  littafin kuwa shine  Usulu Deen shidai  littafin usulu deen  littafine karami (ga takardu)  ammayakunshi duk abindabukata gameda tauhidi. Acikin wannan majalisin shehu yayibayanin siffofin da suka wajaba a siffanta allah da su na daga samuwarsa  da dadewarsa da wanzuwar sa har zuwa karshensu.Yakan ce  dukan Halitta duka fararrace kuma ma haliccinta Allah. Yakance  "MALA' IKU" dukansu tsararrune  basu sa6a wa `Allah´  ga abinda ya umarce su  kuma suna aikata abinda ya umarcesu. su halitta ce  mai haske  su ba maza  kuma ba mata ba;  ba su ci kuma basu DAYA   Sa annan duk abinda yashafi ubangiji  yayi bayaninsa. Hakama yayi bayani akan abinda yashafi   annabawa; da  abinda  yashafi  ranar  Alkiyama Haka  kuma  kowace  matsala tundaga siffofinda suka  can canci a siffanta ubangiji dasu har zuwa bayanin  lahir, kowace matsala  saida ya ambaci  hujjarta daga alqurani  Maigirma. Adubi  littafin Ihyau sunna nasa  a babin imani. Haka kuma  ana iya duba infaku da tar juman dukansu na sarkin musulmi muhammadu bello. Ana ma iya  duba littafin Usulu deen. Abu nabiyu  da yake  bayani  akansa  a irin wannan majalisa  ta waazi  ga masu karamin sani, shine fannin furu´a watau dai Fikihu. Acikin wannana fannin shehu  na karantarda masu sararensa alwala  da yadda ake yinta.  yana kuma koyar da su wanka da yadda ake yinsa. kuma yana koyardasu taimama dayadda ake yinta. Bayan haka  kuma sai  yashiga bayani akan sallah  tare d yimasu bayanin siffar yadda ake yinta. Sa`annan  sai yayi masu bayani  a kan sujadar rafkanuwa. Bayan  haka, sai yayi bayani akkan zakka da matsayinta  da nau o inta har zuwa zakkar fidda kai. Bayan haka sai bayani kan azumi da hajji da yanka da hukunce hukunce rantsuwa da  alkawari, haka kuma yatabo hukunce hukuncen aure da ciniki.  Abin nufi shine shehu yanada majalisar da yake yiwa masu saurarensa  bayani akan abubuwan da suka gabata daga lokaci zuwa lokaci. Awani lokaci yayi bayani akan sallah. awan lokaci yayi bayani kan aure awani lokaci yayi bayani akan  ciniki. Da wannan ne zamu gane cewa  dolene mai waazi  yazama yana tabo kowane sashi awajen waain sa. Bawai matsala guda koyaushe tazama abin tattaunwa ba. Wani abu kuma  da shehu kan yi magana akansa  wanda yake shine abu na ukku  da yakan tattauna akansa  kuma  yayi bayni ga masu sauararensa, shine  fannin sufanci . Acikin irin wannan majalisa  ce shehu kan cewa masu saurarensa, Yana wajaba a kan kowane musulmi da ya tsare kunnuwansa ga sauraren kowane magana  ta wasa da batsa  kuma yatsare ida nunsa  ga duban abinda yake haram. kuma  ya kiyaye harshensa  ga fadar giba  da dukkan abinda bai halattaba. Haka kuma  yatsare hannunsa daga sata da dukan abinda baa yarje masaba da ya aikata  ba. Haka kuma   yakiyaye cikinsa daga sanya masa haram  kuma yakiyaye al aurar sa daga zina da liwadi. Yakiyaye kafafunsa daga tafiya irinta takama  da zuwa wurin sabo. Wadannan  sune gabbai guda bakwai wadanda idan mutum yakiyayesu to yazama mutum salihi  nagari. Acikin irin wannan majalisa ce har wayau  dai shehu ke karantarda masu saurare siffofi na munjiyatu  watau siffofi  masu ku6utarwa kuma masu tseratarwa  ga shiga wuta .Haka kuma  yanayimasu bayanin muhlikatu watau siffofi masu halakarwa kuma su sanya mutum wuta. Munjiyatu sun kunshi tuba  da ikhlasi  da  hakuri da gudun duniya  harma kuma ga dogara  ga allah da fauwala al amari zuwa gareshi .


Zamuci gaba in sha Allah ku kasance tare da mu a Shafin mu na Ma'asuma Nigerian News Update


Real Naseer Umar Alhassan

Na Shaheeda Bawan Allah

2/9/1444. 24/3/2023

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post