TAMBAYA: Allah ya gafarta Malam, ina hukuncin bi ta gaban mutum idan yana salla?




SHAIKH ZAKZAKY: Lalle ba a ruwaito wani hukunci dangane da wannan ba. Saboda haka ratsa salla, sai dai in ana ganin sa ta fuskacin rashin girmamawa ne ga sallar, amma in ba haka ba, lalle bai shafi sallar ba. Tunda cikin ruwayoyi ya nuna har mutum ma a kan jaki yakan zo ya ratsa ya wuce kuma ana salla. Har jaki ma yakan ratsa salla, kuma salla ta yi. Amma abin da 'amah' take ruwaitowa cewa idan mutum ya zo zai ratsa sallarka ka tunkude shi, in ya ki ka yake shi domin Shaidan ne, wannan bai inganta ba. Kuma ba za a taba yin hukunci da shi ba. Kuma ma bisa gaskiya ma ya saba hankali da basira. Da kuma ruwayar da har ila yau 'amah' take kawowa cewa, mace da jaki da bakin kare suna bata salla, shi ma wannan kagaggen hadisi ne, kuma ma ya saba hankali da basira. Don mutum ya ratsa ta gaban sallarka, bai shafi sallarka da komai ba, sallarka kuma na nan, ba abin da ya shafe ta. Kuma ba ruwanka da mai wucewa ta gabanka, saboda sallar tafiya take ruhiyyan ya zuwa ga Allah (T). Ba jiki ne ba, ballantana wani jiki da ke motsi ya tunkude ta ba.

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post