An haramta wa gwamnatoci cire tsabar kuɗi daga asusu a Najeriya....!!!




[ MA'ASUMAH TV// Mnnu/Ng0041 ]


 Hukumar da ke yaƙi da laifukan da suka shafi hada-hadar kuɗi a Najeriya, NFIU, ta ce dokar hana cire tsabar kuɗi daga asussan gwamnati a kowane mataki za ta fara aiki daga ranar ɗaya ga watan Maris mai zuwa.

A cewar hukumar Nigeria Financial Intelligence Unit (NFIU), duk wani jami`in gwamnati da ya taka dokar zai fuskanci ɗaurin shekara uku a gidan yari ko kuma tarar da za ta kai ninkin kuɗin da ya cira sau uku.

Shugaban NFIU Malam Modibbo Hamman Tukur ya faɗa wa BBC Hausa cewa tun daga lokacin da gwamnatin Buhari ta fara mulki an cire jimillar garin kuɗi naira biliyan 225 daga asusun gwamnatin tarayya.

"Gwamnatocin jiha ne suka fi cirar kuɗin, inda aka ɗauki garin kuɗi biliyan 700. Gwamnatocin ƙananan hukumomi kuma biliyan 156 kawai suka cira," in ji shi.

Danna hoton ƙasa ku saurari cikakkiyar hirar da Ibrahim Isa ya yi da Malam Modibbo:



Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post