Jami’an tsaro sun aukawa zaman juyayin Ashura na yau Asabar a Kaduna….

Rahotanni da suke shigo mana yanzun sun tabbatar da cewa jami’an tsaro sun aukawa ‘yan uwa dake gabatar da zaman juyayin Ashura a yau Asabar a rana ta uku ke nan da fara wannan zaman na bana a garin Kaduna.


Rahotannin sun ci gaba da bayyana cewa jami’an tsaron sun yi amfani da hayaki mai sa kwalla sannan kuma suka yi harbi da harsasai masu rai akan masu zaman juyayin wadanda suka hada maza da mata da kuma kananan yara.


An nuna cewa akalla mutum daya yayi shahada sannan kuma wasu da dama sun jikkita sakamakon wannan harin da jami’an tsaron suka kai.


Shi dai wannan zama ana gabatar da shi a fadin Nigeria da sauran kasashen musulmi na duniya.


A ko wacce shekara a cikin watan farko na Muharram al’ummar musulmi suna juyayin abin daya faru na kashe jikan Manzon Allah[SAWA] watau Imam Hussain[AS] a shekara ta 61 bayan hijirar Manzon Allah[SAWA].


SOURCE: https://harkarmusulunci.org/

DOMIN CIGABA DA SAMUN LABARANMU KU BIYO A SHAFUKAN SADA ZUMUNTA NA 


@FACEBOOK: https://web.facebook.com/Maasuma.com.ng/

@TWITTER: https://twitter.com/MaasumahNews/

DOMIN BAMU SHAWARA KO AIKO MANA DA LABARI KUYI MAGANA TA ADRESHIN

@EMAIL: maasumalabari@gmail.com 


ZAINILABIDINA AHMAD SULEIMAN

My Name is Zainilabidina Ahmad Suleiman Chief Executive Officer CEO Bz News 24/7. Famous Blogger| Developer | Programmer| Journalist| Consultant |Publisher |. Contact bzglobalservice@post.com Whatsapp+2348133888333

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post