DABBOBI MA SUNA DA HAQQOQI AKAN MU!!

MA'ASUMAH NIGERIA NEWS UPDATED

__________________________________________

-Manzon Allah (S) yace, "Dabba tana da hakkoki shida (6) akan mai ita,

1- Duk lokacin dakai aiki da ita, dolene ka barta tai kiwo (taci abinci).

2- Dole kabata daman shan ruwa duk lokacin da kuka zo gifta wajen da ruwa yake.

3- Bazaka dake ta ba harsai ana bukatar hakan (ya cancanta, yazam dole).

4- Kada ka zuba mata kayan da yasha karfinta.

5- Karka saka ta tafiya mai nisan da bazata jure ba.

6- Kuma kada kake daukar dogon lokaci baka barta ta huta ba."

-A wani Hadisi kuma Manzon Allah (S) ya kara da cewa, " Kar ka doki dabba a fuska sabida lalle suna yabo ga Allah dayi masa tasbihi."

-Manzon Allah ya kara da cewa, " Ba wata dabba, koda kare ne da za'a kasheshi ba tare da hakki ba, face saiya kai karar mai kisan ranar alkiyama"

ΦΦΦΦΦΦΦΦΦΦΦΦΦΦΦΦΦΦΦΦΦΦΦΦΦΦ
-Mustadrak Al-wasael Bugu Na 8, Shafi Na 258.
-Al-kafi Bugu na 6, Shafi 538.
-Kanz Al-Ummal Shafi 39968

__Bin Haroun Sigau√__

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post