Kalamai masu tsoratarwa dangane da yadda mutuwa ke kusanto mu duk Sekwan!!!


➝Daga βιπ 卄α尺ουπ 丂ιᎶαυ

🇨🇮 Ma'asumah Nigerian News Update.

Wadannan zantuka ne na Imam Ali (As) da aka kawo cikin littafin Gurar Al-hikima, dangane da mutuwa.

1- Duk lokacin daka kusanto mutuwa, ka kyautata ayyukan ka akan na da.

2- Ga dukkan lokacin da ake tsammani akwai ranar da za'a kai ga abin tsammanin.

3- Ga ko wanne mutum akwai ranar da zai tafi kuma bazai sake dawowa ba.

4- Ga ko wanne mutum akwai direba dake tuka shi zuwa ga mutuwarsa.

5- Inda zai zam ana ganin kusanto war lokacin mutuwa da kowa ya ringa tona dukkan sirrin sa. 

6- Idan da zaga mutuwa tana kusanto ka, hakika, zaka tsani rikici da yin karairaku

7- Idanu zaka ke tunani akan kusancin ka da mutuwa, da tanar zuwanta. Jin dadi da wakwakar duniyar ka zai kau.

8- Duk wanda yake mai kiyaye wa da mutuwar sa, zai zam mai karancin tammani.

9- Wanda yaki daukar duniya madauwama, zai zamodaga cikin masu karancin buri.

10- Wanda ya kyautata ayyukan sa baida burin da ya fice mutuwa.

11- Wanda yake kirga gobe a matsayin cikin rayuwar sa, bai bawa mutuwa muhallin da yac da ita ba.

12- Menene maganin da yafi komi! Shine; mutuwa!

13- Babu garkuwar da ke bada kariya kamar lokacin mutuwa.

14- Babu abinda yake na gaskiya kamar mutuwa.

15- Kai abin gurbi ne, sabida an saka maka lokacin mutuwa, kuma mutuwa kullum haru take kawo maka.

16- Amincin Allah ya tabbata ga wanda ya gane dukkan kwallin numfashin sa yana kara kusanto dashi ga mutuwa ne, don haka yayi hanzarin kyautata ayyukan sa na gargaru

17- Rahmar Allah ta kara tabbata ga mutumin da ya karyata tsammanin sa, ya kuma kyautata ayyukan sa.

18- Wasu lokatun mutuwa takan buya karkashin tsammani.

19- Da shudewar awan ni, rayuwa ke karewa.

20- Hakika, akwai garkuwa gare ni, ta wajen batun mutuwa ta, in lokaci yayi garkuwar da kanta zata kauce ta bayar a dauki raina.

21- A wannan lokacin kibiya bazata kauce wa sauti abin hari ba, rauni kuma bazai warke ba.

Wa iyazu billah.😭
 'Yan uwa mu gyara Alaqarmu da Allah domin mutuwa ba sallama take ba.

Allah ka kyautata karshen mu, kasa muzam cikin Shaheedan Karbala.

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post