No title

CIGABA DA ZAMAN MAKOKIN ASHURA  A GARIN DAURA

Yau Litinin 9 watan Muhrram shekarar ta 1441AH  yan'uwa musulmi almajiran Sheikh Zakzaky (H) suka cigaba da zaman tunawa da musibar da ta sami Imam Hussain (A.S) da sauran zuriyyar Manzon Allah (S) shekara ta 62 bayan Hijira.

Mallam Mustapha muhamad ne ya jagoranci zaman inda ya karantu yadda kwamandojin sojin Yazidu (LA) suka fara kada kugen fara yakar Imam Hussain (AS) dan Fatima az Zahra diyar Manzon Allah (s.a.w.a.). Imam Hussain ya kira dan’uwansa Abbas a daidai wannan lokaci yace masa “ya Abbas! kaje ga kwamandojin sojojin Yazidu, ka tambayesu su yi mana Karin jinkirin dare daya, har zuwa gobe”.

#Ashura2019
#LabbaikaYaHussain
#FreeZakzaky.



Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post