NIMA MUTUM DAYA DA RABI NAKE DASHI.

Daga wakilin shafin Ma'asumah Nigerian  News Updates.   --Idishia Jos.

 A shekaran jiya Asabat ne 27/4/2019 da yammaci muka ziyarci su Allama Ibraheem Ya'qoub El-Zakzaky(H) a inda ake tsare dasu tsarewar da ba bisa ka'ida ba a garin kaduna. Bayan an gaisa sai su Malam(H)suka fara bayani da cewa"Assalamu alaikum nasan kun san likitoti sun zo dubamu. Tun muna Abuja maganar kawo likitoti daga waje take, basu bayar da wannan daman ba, har sai da suka kawo mu kotu anan kaduna sannan shi Alkalin da yake shari'a din yace zamu iya zuwa da likitoti daga ko ina ne, domin su dubamu.
       To dama a baya da muna Abuja munje Asibiti daban-daban da farko kafin aiki(aikin ido) ina gani aka zo akai aiki sai ina gani dishi-dishi aka sake aiki sai ban ma ganin na kusa, na nesa, kuma ban ma gani sai yanzu da aka mun 'Glass' nake iya karatu shima sai na kawo kusa(ya misalta mana yana me matso da tafukan hannayensa kusa da idanunsa)  .
       To sai shi likitan su(DSS) yace wai Trauma (rauni) ne, nace a'a ya zaka ce haka bayan kayi man aiki ina gani amma bayan aikin sai ban gani, sai nace ina bukatar ganin wani likita, sai suka kai mu wani Asibiti na hadu dashi nace ban yarda a dubani da karafunan su ba, dan kwanaki sun hanamu ganin likitotinmu har nake cewa waye ne a saman daya hanamu(ganin likita) saboda mu san shi, dan nan gaba zamu rama, mu san wanda zamu rama akan sa idan mun tashi ramawa.
    Likita ya taba rubuta wadansu sunayen  kayayyakin aiki wadanda za a nema kafin ai aikin aka bawa (wata mata me kula da sashin lafiya a hukumar tsaro ta farin kaya) sai taje ta ajiye takardan acan kasa a ofis shekara daya ba suce mana komai ba, da aka sake magana sai tace bata ganshi ba, To dama akwai copy sai aka sake basu".

  Su Malam(H) suka cigaba da cewa "Jiya mun je dasu(likitotinmu da suka zo daga kasar waje)  Asibitin ido, mun wuni acan har zuwa dare, sai kusan 10:00pm sannan muka koma gida, sun kuma yi duk gwaje gwajen daya kamata yanzu dai abinda ya rage kawai shine result (sakamakon bincike)".

"Da su mahukumta sun ce ne wai sai dai aje damu Abuja can ne za a duba mu, sai muka nuna masu sam bamu yadda suyi hakanan ba, akan me za a kaimu Abuja?  Sai  an yi awanni ana tafiya ga hanya babu kyau ga Madam tana fama da kafa ayi ta faman zagwan zagwan a hanya. Suna da wata manufa daban(shiyasa suka ce aje can Abuja ayi gwaje gwajen), suna so su birkita kayan aikin da suka zo dashi ne(kayayyakin aikin da likitotinmu suka zo dasu daga kasar waje). Sun so su kawo cikas su hana abin, to abu nan da nan sai ya yadu(cewa an hana likitotin da suka zo daga kasar waje ganin su Malam ) to ina jin sakamakon abinda akayi ne(Muzahara) sai suka ce to to mun yadda a duba ku anan(garin kaduna maimakon Abuja)".
       
  "Akwai likitan ido acikin su(likitotinmu  da suka zo daga kasar waje)  shi da yayi 'scanning' din idon nawa sai ya gano akwai karafunan gutsasin harsashi mai guba a wannan idon(hagu) da ma wannan(dama) ni ban sani ba ashe ina yawo da karafunane acikin idanun, wanda shi likitan 'security' sai da aka kwashe shekara biyu sannan ya iya gano karfe guda daya a idon, ashe suna ta boye min ne(DSS)  akwai guda aciki".

Wani bangare na hotunan likitocin da suka duba lafoyar SHEIKH ZAKZAKY (H) a satin da ya gabata.



"Nima mutum daya da rabi nake dashi!  Su Malam(H) suka juyo da fuskarsu gareni suka tambayeni cewa "Kasan kissar mutum daya da rabi?  Na gyada kai nace a'a Malam, Sai suka juya da kansu suka kalli sauran maziyartan suka yi tambaya, suka ce ''kuntuna da kissar mutum daya da rabi? Kowa yayi shiru yana raba idanu alamu dai ba a sani ba, Sai su Malam(H) suka ce "aikuwa nasha bada labari akan mutum daya da rabi, wani shirine na kalla a talabijin ba drama(Wasan kwaikwayo)bane domin shi a stage(dandali) ake yin sa amma wannan film ne ban sani ba ko ya faru da gaske, wani shaikh ne aka kai karansa wajen sarki, aka cema sarki ranka ya dade shaikh yana so yasa mutane suyi baka bore, dan ya ga mutane suna tare dashi, bayan an tashi daga fada, sai sarki ya kira bafadansa yace ina so kaje ka kamo shaikh ne kai kadai lokacin da zaka kama shi ka tabbata babu wanda ya ganka, to bayan an idar da sallar subahi an fiffito an raka liman mutane sun watse sai kawai bafade wuf ya kama shaikh ya tafi dashi fada wajen sarki, sai sarki yace wa shaikh  an ce kana tara mutane za ayi min boye sai shaikh yace ni?  Ai ni bani da mutane ni mutum daya da raba kawai nake dashi,  sai sarki yace mutum daya da rabi bangane mutum daya da rabi ba.  Sai shaikh yace kana so kaga mutum daya da rabinne?  Sai sarki yace e, yace to ka tara mutane kace ka kashe ni ko kuma zaka kasheni to zakaga wannan mutum daya da rabin,  sai kuwa sarki yasa aka tara mutane  aka sanar cewa an kashe shaikh sai ga yaron shaikh ya fito yana cewa tunda ka kashe babana to nima gani ka kasheni, aka rirrikeshi yana ta fisge fisge yana cewa shima gashi a kashe shi, sai sarki yace ma yaron ka kwantar da hankalinka ba a kashe ubanka ba, to dama an sanya labule a wajen shaikh yana bayan labule yana makale, sai shaikh ya fito sai wani daga cikin almajiransa yace Alhamdulillah ala salamatuka(mun godewa Allah daya kubutar da kai), nima ina tare da kai.  Sai shaikh ya cewa sarki to wannan Dana shine mutum daya, rabin kuma shine almajiri".
  Sai su Malam(H) suka cigaba da cewa "wadanda suka tsaya kyam suka dake suka jajirce sune nawa, suma wadanda suka yi likimo suma dai duk nawane(dariya). Muka kwalla salati.

Su Malam(H) suka cigaba da cewa 'yan likimo su je su cigaba dayin likimo abinsu, amma abu guda muke roko daga garesu, su yi shiru da bakinsu.  In me motsi ya cewa me likimo zo muje muyi motsi sai yace shiiiii(🤫)  addu'a addu'a za ayi(dariya)".


An bawa su Malam(H)  labari akan yadda Muzaharan Nisfu sha'aban ta kasamce, da yadda 'yan majalisa suka ki turo wakili domin ya karbi kokenmu, har daga karshe aka kai ga girgije kofar shiga majalisar, aka balle kwadon aka shiga ciki.
     Sai su Malam(H)  suka ce "Majasila gidan kowa da kowane, su 'yan majalisa suna wakiltan mutane ne. To mutum zai dawo gidan sane Dan mukulli gidan ya bace sai ya je round about ya kwana? Ai zai gyara kofan ne.  Ai suma('yan uwan da suka girgije kofar suka balle kwadon kofar shiga majalisar)  gyara kofar suka yi suka shiga dama gidan sune(dariya)".
  Aka cewa su Malam(H) amma wasu 'yan uwa din sunata faman surutai akan balle kwadon majalisa suna cewa wannan ba koyarwan su Malam(H) bane.  Su Malam(H) suka amsa da cewa"kasan wasu mutanan su kodayaushe suna yin tunani negatively(gajeran tunani)".
   
Aka cigaba da bawa su Malam(H) labari rashin fahimtar da aka samu tsakanin  Harisawa 'yan traffic da kuma wasu Matasa a yayin gudanar da Muzaharan Nisfu Sha'aban a Abuja, ta yadda aka ce su 'tan traffic sun shiga gaban 'Banner' suna karewa wacce ita banner din tana dauke da sakon dalilin fitowa Muzahara din, har ta kai ga an samu rashin jituwa a tsakani, Sai su Malam(H)  suka ce"Ba dai harisawa ba sai dai 'yan security ma'aikatan gwamnati,  kuma tun lokacin da aka fara wannan motsin suna ina? Sai yanzu ne za su zo da wannan".  Sai aka cewa su Malam(H) sun ce  wai haka ake yi ko ina a duniya.  Sai su Malam(H)  suka ce suka ce"To idan haka ake yi ko ina a duniya, to mu ba hakanan muke yi ba. Sai su je inda ake yi duk duniya suyi irin na 'yan duniya(dariya), mu nan ba haka muke yi ba, namu daban ne".

   
"Da nayi magana akan 'yan business free zakzaky company limited nasan basu daina kasuwancin ba,  amma jarin nasu yanzu tayi kasa(dariya).  Akasarin kudaden da suke samu ba a wajen 'yan uwa bane, a wajen 'Sympathizer' ne (masu nuna goyon baya akan harka)".
   
"Duk abinda yake faruwa a waje nasani nayi musu shiru ne, naga abinda zasuyi idan na mutu! Wasunsu sun san nasan abinda suke yi,  kokarinsu shi ne kada 'yan uwa sugane nasan abinda sukeyi".

Su Malam(H) suka waigo da fuskar su gareni suka fara yi min magana da cewa"Da yake ana yin tsaraba idan an zo wajen Malam 'yan uwa sun saba, ko da an ce musu da aka je(ziyara) su Malam(H)  sunyi shiru ne basu ce komai ba,  ('yan uwa) ba zasu yarda ba. Kun rubuta tsaraba akan 'yan business wani daya karanta sai yace wannan haukane, ba hikima aciki,  shi a wajensa wannan ba hikima bace,  saboda ba a fadi son ran sa ba.  Allah yayi magana mutum ya ji yace haukane, to ka kwatanta girmanka dana ubangiji(zai yiwu ka kwatanta kanka da Allah?  Ba zai yiwu ba) .  Nima lokacin muna waje ba a tsaremu ba,  idan nayi magana sai ace ai ba a gane maganan malam sai an yi muku fassara, gashi kuma ni da Hausa nake magana bada canis  ba..  kasan me yasa haka suke cewa haka?  Nace a'a Malam,  sai suka ce "saboda suna so su murguda maganan ne.  Tsaraba (da kuke rubutawa idan kun ziyarce mu) yana amfanar wanda zai amfana saura kuma sai suje suyita kunaguni, da yake yanzu lokacin Internet ne".
    Da naji wadannan zantuka na rarrashi daga su Malam(H)  sai na kara samun kwarin gwiwa akan gudummuwar da zan iya badawa. Muka yiwa su Malam(H)  rakiya zuwa waje da yake magriba ta kawo jiki, mukayi sallama dasu.

Sayyid Badamasi tare da likitocin da suka duba lafiyar Sayyid Zakzaky (H) a makon da ya gabata 

-Ya'qoub Badamasi El-Zakzaky.

-Aliy Haidar Badamasi.

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post