Aƙalla Mutum 50 Suka Rasa Rayukansu A Wani Hari Da Isra'ila Ta Kai Wani Masallaci A Gaza.



Daga - Mahadi Tukur Almizan.

Kimanin mutum 50 ne suka yi shahada a wani hari da haramtacciyar ƙasar Isra'ila ta kai kan wani masallaci a jiya Laraba 15 ga watan Nuwamba kamar yadda kafar yaɗa labarai ta WAFA News Agency ta ruwaito.

Isra'ila ta kai wannan hari ne a masallacin dai dai lokacin da ya ke cike da Palasɗinawa Musulmi a yayin da ake sallar Jam'i a Masallacin na Ihya - Ussunnah. 

Wannan dai ba shine karon farko da Isra'ila ta kai hari muhallin ibada ba, Isra'ila ta kai hare hare mabanbanta a Masallatai da Coci Coci tun daga fara wannan yaƙi.

Ko a ranar 20 ga watan Oktoban da ya gabata, haramtacciyar ƙasar Isra'ila ta kai hari Masallacin Al-Omari da ke Jabalia, wanda wannan masallaci yana daga cikin manyan Masallatai a Palasɗinu.

Kafin wannan hari na Masallacin Al-Omari Isra'ila ta kai hari Cocin "Saint Porphyrios" dake Gaza, wannan Coci itace Coci ta uku a Coci mafi daɗewa a Duniya baki ɗaya.

A sakamakon wannan hari kan Coci ƙungiyar "World Council Of Churches" ta fitar da sanarwar Allah wadai da ta'addancin Isra'ila a Gaza, kuma ƙungiyar tayi kira ga al'ummar Duniya wajen baiwa asibitoci, makarantu da wuraren Ibada na Palasɗinawa kariya.

✍️ Mahadi Tukur Almizan | Ma'asuma Nigerian News Update

Zaku iya samun datar kowane Network cikin sassauƙan farashi a FADAKDATA



1 Comments


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

  1. Ya Allah ka daukaka musulinci da musulmai,ka danne kafirci da kafirai da masu Goya masu baya,ya Allah.

    ReplyDelete
Previous Post Next Post