Falalar Son Sayyida Fatima Azzahra Ummush Shurafa(A's)....!!!


[ MA'ASUMAH TV// Mnnu/Ng0041 ] 


Akwai hadisai masu yawa da aka ruwaito daga Manzon Allah(S)

Kan Falalar Son Sayyida Fatima (a,s) Ga wasu

Daga cikin hadisan:

1-Manzon Allah ya ce, 

“Duk wanda yaso Fatima ‘ya ta to zai kasance cikin

Aljanna tare da ni.” 

A wani hadisi kuma Manzon Allah(S)

 ya ce, “Son Fatima yana Amfanar mutum a

wajaje Dari daga cikin wajajen Akwai lokacin

mutuwarsa,  zamansa A kabari,  Ranar kiyama,kan siradi da kuma wajen Hisabi.

A wata Ruwaye ya zo

Akan cewa son Fatima Alama ce ta Imani, kinta

kuma Alama ce ta munafirci.

A wata ruwaya

kuma Manzon Allah(S) ya ce, “An sanya ma Fatima

suna Fatima domin Allah ta’ala ya Bata Damar Fansar Masoyanta Daga Wuta Zuwa Aljannah.


Tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gareta, tare da mahaifinta, da

mahaifiyarta da mijinta, da ƴaƴanta.

 


1 Comments


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post