■ Duk Tsananin Da Katsinci Kanka To Ka Tuna da Jagoran ka..!!!



@Ma'asumah Nigeria News Update 


A duk lokacin da katsinci kanka acikin wata musifa a gwagwarmayar nan to lallai kayi tunani da irin halin da jagoranmu sayyed zakzaky (H) yake ciki.

Mas'udu Dan masani Shinkafi 

Katuna yadda azzalumar Gwamnatin Nigeria ta dirarwa sayyed zakzaky ba tare da yayi masu laifin komi ba illa kawai dan yace yana son annabi da iyalansa tsarkaka (as).


Su buhari suka kashe masa zaqaquran haziqan 'ya'yansa har guda shida duk a gaban sa, sannan sukayi masa ruwan harsashi, shida matansa


Suka rushe dukkan muhallansa mallakinsa, sannan suka rushe kabarin mahaifiyarsa kamar su tonota.


Suka kashe masa almajiransa sama da Dubu daya 1000+.


Haba dan uwa kai mutum nawa aka kashe maka?? Gida nawa aka rushe maka??, 


To idan mukayi duba da abinda yasamu jagoranmu zamuga cewa lallai mu duk abinda akayi mana mai sauqi ne akan abinda akayiwa jagora, ko kuma ince ake kanyi masa.


Ya ubangijin mazalumai Ka saka mana akan ta'addancin da Buhari yayiwa sayyed zakzaky (H) da almajiransa

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post