Dandalin Matasan Yankin Jos, Ta Karrama Sheikh Adamu Ahmad Tsoho, Malam Ibrahim Tahir Gyallesu, Da Wasu Zaqaquran Mambobinta



An karrama Shaikh Adamu Ahmad Tsoho da takardan lambar yabo da girmamawa. 

Inda shugaban Dandalin Matasa na Yankin Jos; Malam Musa Umar Chajj-Chaji ya miƙa masa a madadin Matasan Harka Islamiyyah. 


Sannan kuma ta baiwa Malam Ibrahim Tahir Gyallesu lambar jinjina ta musamman a gareshi da yayi Tattaki tun daga Zaria, ya jagoranci Zikiran Tunawa da Shahidan Dandalin Matasa na Yankin. Sheikh Adamu Ahmad Tsoho ne ya miƙa masa. 


Ta karrama wasu ɗai-ɗaikun Mambobinta, da kuma yankuna da suka haɗa da; Jos, Saminaka, Lafia, Keffi, Doma, Gumau da Doguwa. Sheikh Yusuf Abubakar ne ya miƙa musu lambar girmamawar.   







An karrama su jiya Lahadi 30-May-2021, a wajen taron Ƙarawa Juna Sani (Mu’utamar) karo na 10 a garin Doguwa.


#DoguwaMuutamar2021

#DandalinMatasaJosZone


— Muh'd Jawad Assaminaky

     @ Media Forum Saminaka

21-Shawwal-1442H. 31-May-2021.

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post