Talakawan Nigeria ko Kuna So Ko Bakwa So Sai Gwamnatin Buhari Ta Inganta Rayuwar ku !!!


............................................................
..................
... Umar Hassan Gololo...
Da can Kun San mu ne kuka zabemu.?
Mune muka ce muku mu masu gaskiya da rikon Amana ne kuka yarda amma ai baku taba bamu amanar kuka ga bamu ci ba ko.?
Hatta Mutanen da muka dauko suka Zama Ministoci da wadanda suke rike da manyan mukamai ba kune kuka zabesu ba mu da kuka dauka masu gaskiya ne muka zabesu to me kuke tsammani daga garemu.?
Saboda haka dukkan abinda muka dama haka zaku Sha idan ya muku ku karba,idan bai muku ba ku zuba mana na mujiya..
Abu guda daya da bama wasa dashi shine shigar kudade aljifanmu.
Don haka duk halin da kuka shiga na bala'in yunwa, rashin tsaro da tashin gwauron zabi na kayan masarufi duk cikin aiki ne.
Dole ne ku Sha wahala mu musha dadi duk domin inganta rayuwarku..

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post