YANZU-YANZU : Jami'an Tsaro Na cigaba da bude wuta akan 'Yan Shi'a Masu Taron Ashura a Cikin Garin Kaduna da Zariya, Bisa Umurnin Gwamnan Jihar Kaduna Nasiru Elrufa'i




Muzaharar Ashura: An Raunata Mutum Hudu A Kaduna

Jami'an tsaron Nijeriya sun afkawa 'yan'uwa Musulmi almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) masu muzaharar #Ashura1442 a garin Kaduna a halin yanzu.

Ya zuwa karfe 3 da mintoci 12 na yammacin yau Lahadi, sun harbi 'yan'uwa akalla mutum hudu wadanda aka iya tantancewa a yanzu. A yayin da daya daga cikinsu kamar yadda majiyarmu ta tabbatar an harbe shi a kai ne.

Sai dai masu muzaharar duk da ruwan harsasai masu rai a kawukansu, sun samu sun karasa Junction na Leventis inda suka rufe Muzaharar sannan aka sallami 'yan'uwa kowa ya fara watsewa.


Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post