LABARAN DUNIYA: TASHIN BOM A JAHAR KATSINA

Bama-bamai sun hallaka mutane 5 da jikkata 6 a jihar Katsina

Wasu bama-bamai sun tashi a kauyen Yammama, dake a  karamar hukumar Malumfashi ta jihar Katsina kuma mutane da dama sun rasa rayukansu.

Daily Trust ta ruwaito cewa wannan abu ya faru ne a yau Asabar a gonar wani mutum mai suna Alhaji Hussaini Mai Kwai, in da mutane
5 suka rasa rayukan su yayin da aka garzaya da 6 zuwa asibitin Malumfashi da ke jihar.

Wani da abun ya faru a gaban sa kuma ya nemi a sakaya sunan sa yace wadanda suka mutu leburori ne dake yin noma a  gonar.

"Na kirga gawawwaki 6 kuma an garzaya da wasu 5 asibiti. Jami'an tsaro sun killace wajen yanzu." Majiyar ta ce.

Da aka tuntubi jami'an yansanda akan lamarin, Jami'in hulda da jama'a na Rundunar Yansandan Jihar, SP Gambo Isaha , yace sun tura jami'an su a wurin da abin ya faru domin gudanar da bincike.

Allah shi kyauta ya kuma kawo mana zaman lafiya mai dorewa

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post