Zalunci da kisan da ake wa yan shi'a, yasa na fahimci kiran Zakzaky!!!

Firar wakilinmu Bin Haroun Sigau, tare da wani sabon fahimtar wannan kira na Allama Sayyid Zakkzaky (H).

🇳🇬 Ma'asumah Nigerian News Updates.

A firar tasu wakilinmu yake tambayar sa cikin wasa da raha, yakai dan uwa me ya sa ka harka fahimci wannan tafiya a  lokacin da ake fiskantar waki'o'i (kisa da kamu)?

Dan uwan yake cewa, "Ai mu waki'ar muka gani mu biyo, domin badon waki'ar ba da kila bamu fahimci wannan kira ba. Mun fahimci wannan tafiya ne bisa ganin jajircewa da kuma sadaukar darai da ake kan addini, kamar yadda sauran manyan bayin Allah sukai a zamunan da suka gabata. Hakika munyi duba ga dukkan sauran Maluma kuma sam bamu ga kmaar Malam Zakzaky ba, domin kiran sa sak kiran Mujaddadi Usman Bin Fodio, wannan yasa ka muga cewa lallai, wannan tafiyar damu za'a yita".

Daga karshe suka saka na wakilce su don gaisawa da Manyan jagogorin tafiya na garin Lere da Sigau m, tare da gabatar dasu da kuma garin da suka fito.

Sharhi
-----------

A zahirin gaskiya, wannan harka kayar Allah ce, kuma shike zaban wanda yaso, ya kuma fahimtar dashi wannan kira na Manzon Allah da iyalan gidan sa. Ki kokonto bama yi kan wannan kira babu mai kasance wa cikin sai dan hakas wanda yacibyasha daga ciyarwa na hakas kuma aka sameshi ta hanyar hakas.

 Domin ko ba komi nayi zaman aji da wannan bawan Allah, tare muka kammala makarantar gaba da 'Primary' dashi kuma nasan wanene shi, mutumin kirki ne kuma yana da tsantseni wajen kiyaye dokokin Allah (T).

Tabbas aikin halak sai dan halak, wannan harka bata tara mutanen banza ba, hasali ma gyara wadanda suka kauce take yi, ta maida wanda bau san ma kansa ya gane kansa da kuma hanyar da zaibu mikakkiya takai shi ga Manzon Allah (S).

Inda zaka saka yan uwa a mizani, zai zamana in ka saka shi a cikin mutanen dake kewaye dashi zaka ga mutum ne na kwarai, kuma zaka gan duk da hakan ya fi sauran aklaq.

Sai nake ganin muna da wata nakasu guda, wanda ke hana ma wannan da'awa kaiwa wasu wuraren. Naqasun kuwa shine wasun mu basu son bayyana kansu cikin mutane bakin fiska, duk da zaka ga wasu kana da akaqa dasu mai kyau, da sauqin fahimta.

Saika ga daga baya wani Abokin ka ya fahimci harka amma baima san kai dan harka din bane.

Kamar yadda naga hakan ya faru da wasu mutum biyu, a jami'ar Ahmadu bello dake Zaria. Suna aji daya saida suka kai shekarar karshe suka san su yan uwa ne mabiya Sayyid Zakzaky a wajen taron tarbar sabbin dalibai da Afimn ta shirya.

Kaga wannan ai abin kunya ne, gskiya yanzun ba muna lokacin boye kai bane, domin matuqar kai dan wannnan harkar ne, koka bayyana kanka ko kada ka bayyan ana biye dakai da dukkan zirga-zirgan ka a gida kake ko a makaranta domin bazaka taba iya boyowa ba.

Don haka abinda ke gabanmu kawai shine aiki don Allah, bawai tunanin boye kaine zai saka ka tsira a wajen azzalumai ba fatan zamu gyara mu tsayu don ganin addini ya iko damu, ya zam shine tsarin dake jan ragamar zukatanmu.

Wannan fira anyi ta ne ranar Muzaharar juyayin kisan Imam Husain (As) daya gudana a garin Lere, ta jahar Kaduna #Ashura1441.

ALLAH YASA MU DACE....

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post