Yadda Muzaharar Maulidi ta gudana a garin Ramin Kura, yankin Saminaka

Rufe Muzaharar maulud din Manzon Allah a garin Ramin kura, yankin Saminaka dake jahar Kaduna.

🇳🇬 Ma'asumah Nigerian news Update, tare da Bin Haroun Sigau.

A yau ne Juma'a  29 gawatan Nuwamba, 2019.

Yan uwa na garin Ramin Kura suka gabatar da mauludin Manzon Allah a garin na zango mai tsawo.

Bayan an kammala Muzaha din an jaddada kira ga Gwamnati kan ta saki Sheikh Zakzaky bisa umurnin kotu.

Daga karshe Malam Atiku wakilin yan uwa na garin Raamin kura din ya fara jawabin rufewa, tare da bawa yan uwa hakuri bisa tafiyana dogon zango da akai.

Kana malamin ya kara jadda dawa mutane cewa; akwai Mauludin zama da daddare.

Malamin Yake cewa; " Gabar sun sami sauyi daga ashura, kamar yadda muma a wannan kasar aka bishe hasken musulunci dashi kansa manzon nan, aka nuna mana cewa shi wannan Manzon ma mutum ne kamar kowa."


A cikin jawabin nasa yake bayanin cewa; hakika, wannan manzon yana nan daram a zuciyoyin mu wanda wannan Manzon shine ya kawo mana hasken daya haskake zuciyoyin mu muka bar bata muka kama hanyar shirya.

Kamar yadda Manzon Allah yazo a zamanin jahiliyya suna kashe kawukansu da zama cikin rudu, Manzo Allah bai gushe ba saida yaga kowa ya sami yanci, domin shine shafiun nasi, kuma shine kairun nass."

Mun tsakuro wannan dan kadan din ne daga cikin jawabin rufewa muzaharar.


Allah ya kara mana son Manzon Allah.



Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post