TA'ADDANCIN ZARIA

Yau 11-4-2019 shekara ukku Kenan SSG Na Kaduna State, Lawal Babalare Abbas

Yafada DA bakinsa cewar,

SSG Na Kaduna Ya Tabbatar Da sun bizne Gawarwakin Musulmi 347 Da Sojoji Suka Kashe A Zariya
SSG Na Kaduna State, Lawal Babalare Abbas ya tabbatar ma da kwamitin Binciken kisan kiyashin da Sojojin Nigeria suka yi a kan yan uwa Musulmi A Garin Zariya da cewa sun bizne gawarwakin da Sojojin suka kashe a Gyallesu, Husainiyyah da Darur Rahma a Unguwar MANDO da ke bayan garin Kaduna.
SSG ya kuma tabbatar da cewa Gwamnati ta sa an birne gawarwakin Musulmin ba tare da an musu Sallah ba ba kuma tare da izinin majibintansu ba, amma an bizne su ne a gaban Daraktan Kula da harkokin Addinin Musulunci na Gwamnatin Kaduna, da kuma Wasu wakilan Sojoji.

Har ila yau, SSG ya Tabbatar da cewa da izinin Nasiru El-Rufa’i ne aka rushe gane ginen Yan uwa Musulmi tare da gidajen da ke makwaftaka da su don gudun cutuwar al'umma.
Da aka tambayeshi Ko zai fadi yawan gawarwakin da suka rufe a Mando? Sai SSG ya bayyana cewa gawarwaki 191 an daukosu daga barikin sojoji na Deport, Sai kuma gawarwaki 156 an dauko su daga asibitin Shika.
SSG na gwamnatin Jihar Kaduna ya tabbatar da sun birne gawarwakin wadanda sojojin suka kashe akalla mutum 347.

®11-4-2019
©IBNSAGIR

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post