Masu ganin cewa addini Musulunci baya tabbata sai in Mahadi yazo, Waya cema katsaya jiran Mahadi..?, a wane hadisi ne akace idan addini yayi rauni kajira Mahadi yazo..?_Inji Sheikh Zakzaky (h)

Isma'il Abubakar Idris Katsina.

Cigaban Jawabin Sheik Ibrahim Zakzaky kashi na (04), mai suna (Tabbatar Addini) na 1990.

Masu ganin cewa addini Musulunci baya tabbata sai in Mahadi yazo, waya cema katsaya jiran Mahadi..?, a wane hadisi ne akace idan addini yayi rauni kajira Mahadi yazo..?, wanene yafadima lokacinda mahadi zaizo kana yara ko ka Mutu.

Idan kamutu akan tsarin da bana Allah ba yazaka cema Allah cewa zakayi ya Allah inajiran Mahadi ne inyi addini idan kafin Mahadi yazo Mala'ikan mutuwa ya dauki raika, kana tunanin Allah zaice katafi Aljanna ne sabida katsaya jiran Mahadi.

Masu cewa addini zai tabbata amma ba yanzuba waya gayama idan mun ilmantar da 'ya'yanmu da jikokinmu damun koma kiyama wanene zaisamu wannan ladar aikin mu ko jikokinmu, inda wajen al'amarin Allah ne kamata yayi Kai kafara aikatawa diyanka subiyo bayanka sai jikokinka.

Son rai na Al'umma akan cewa yakamata addinin Allah ya tabbata amma bamuda karfin sabida komi yana hannn Arna sune  keda manyan mukamai da manyan kujeru a Gwamnati. Duk mai mafarkin cewa sai munzama Manyan gwamnati zamu tabbatar da addinin Allah to gaskiya wannan Mutumen bai iya mafarki ba.

Idan ace ayi Lissafi Suwanene ke tafiyar da Kasarnan yanzu Musulmai ne, Shuganan Kasa da Shugaban Sojoji, Kwamishinan 'yan Sanda, Cif Joji, Shugaban Alkalai duk cikarsu Musulmai ne amma miyahana ayi addinin Musuluncin...?. Idan har manyan mukamai a gwamnati kesa ayi Musulunci ai angama mi'ake jira ko sai ansami Masinja da Masu share-share da Lebirori suma yanzu ansamu saura mi ake jiya ayi addinin Allah a Najeriya.?.

Minene ya hana ayi addinin musulunci a Najeriya?, Amsa÷ Abinda ake tayar da kasarnan shi ne ba addini ba kafirci ne domin ayau munwayi gari Musulmai suke tafiyar da wannan tsari na kafirci a Kasarnan, bamu damu akan cewa wanene shugaban kasa ko gwamna ba a'a mundamu akan addinin Allah ne bisa Jagorancin Allah yace, Annabi yace, duk abinda Allah baice ba Annabi baice ba to ba addini bane kowa ke tafiyar dashi.

Duk abinda Musulmi ke jagoranta indai har ba Bisa hanyar Allah da Annabi ya Jagoranci ko minene ba to ba musulunci bane kafircine koda Sunansa Alhaji Wa ne.

Misali÷ idan kaje inda ake tace giya a dafa azuba a kwalba idan Manajan gidan giyar Musulmi sunanshi Alhaji Ibrahim sai ace giya ta Halasta asha...?, idan aka tambayeka miyasa kake shan giya saikace giyar gidan Alhaji Ibrahim ne ta halasta kenan...?.

Idan har zamu maida shan giya halas sabida Alhaji Ibrahim ya dafa ta, to zama iya maida Najeriya kasar Musulunci tunda Shuwagabanninta Musulmai ne.

           Muhadu kashi na (05)

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post